‘Yan bindiga sun yi garkwa da mutane bayan sun kai hari a ƙauyen Tungar Maji dake maƙwabtaka da birnin tarayya Abuja.
Mazauna yankin sun ce maharan da suka kai harin da safiyar Alhamis sun yi awon gaba da adadin mutane da ba a kai ga tantancewa ba, amma wasu na ganin adadin ya kai mutum 20.
“Ba mu yi barci ba da cikin dare. Da safe ne ‘yan banga suka ce an yi garkuwa mutane 20″, kamar yadda mazaunin yankin ya faɗa yayin tattaunawarsa da jaridar Premium Time
Jaridar Premium Time ta ruwaito wani mazaunin yankin da ke cewa maharan sun kutsa ne da tsakar dare inda suka yi ta harbe-harbe na kimanin awa ɗaya sannan suka sace wasu mutane.
Ya zuwa yanzu babu wani bayani game da ko an samu asarar rai ko rauni sakamakon harin.
Jaridar ta ruwaito cewa kakakin rundunar ‘yan sandan Abuja, Anjuguri Manza na shirin fitar da bayani kan abin da ya faru a ƙauyen da ke maƙwabtaka da yankin Zuba dake Abuja.
Harin na zuwa ne ‘yan kwanaki kaɗan bayan rahoton hukumar Kwastam da ta kawo game da mayaƙan Boko Haram sun kafa sansanoni da nufin kai hare-hare a wasu sassa na birnin tarayya.
Daga baya rundunar ‘yan sanda ta ce, ta riga ta sha gaban masu nufin kai harin, ta kuma ba wa mazauna tabbacin babu wani abin tsoro.