Rahotanni daga jihar Borno ya nuna cewa kungiyar Boko Haram sun hallaka sojojin Nijeriya shida a yayin wani hari da suka kai kan sansaninsu da ke jihar Borno.
Sojoji shida ne suka rasa ransu a yayin gumurzu a tsakaninsu da mayakan Boko Haram a jihar Borno. Sun kai harin bazata ne a sansanin sojojin da ke yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya. Daya daga cikin jami’an sojin, ya ce sun yi rashin nasara kan mayakan a fafatawar da aka kwashi fiye da sa’o’i biyu ana yi.
Akwai sojoji sama da 40 da ba a ji duriyarsu ba tun bayan artabun, amma ana ganin sun tsere ne a yayin barin wutar inji wani abokin aikinsu.
A dai daren ranar Asabar aka kai harin, a yankin da ayyukan masu tayar da kayar bayan, suka yi sanadiyyar dubban rayuka da tilasta ma mutane fiye da miliyan daya rasa matsuguni.