Galibin ‘yan gudun hijirar da ke zaune a sansanin Bakassi sun bayyana fatan su na komawa gida domin ci gaba da gudanar da ayyukan noma domin samun abin dogaro da kai maimakon dogaro da dan kankanin kayan agaji da suke samu.
Kazalika mazauna sansanin sun kuma nuna damuwarsu kan makomar ’ya’yansu, wadanda ke karatu a manyan makarantu a Maiduguri ba tare da wuraren kwana ba.
A kwanakin baya ne gwamnatin jihar ta bayyana shirinta na rufe dukkanin sansanonin ‘yan gudun hijira a karshen wannan shekara sakamakon dawo da zaman lafiya a yankuna da dama da mayakan Boko Haram suka mamaye.
A ranar Asabar ne gwamnan jihar, Babagana Zulum ya ziyarci ‘yan gudun hijira na Bakassi, inda ya shaida wa mazauna sansanin cewa za a rufe sansanin, kuma za a ba su tallafin da suka dace don komawa gida.
Iyalan ‘yan gudun hijira daga kananan hukumomin Marte da Goza da Monguno da kuma Guzamala sun kwashe shekaru bakwai suna zaune a sansanin Bakassi sakamakon rikicin ‘yan tada kayar baya.