‘Yan gudun hijira fiye da dubu 50,000 daga jihohin Arewa maso gabas dake zaune a jihar Bauchi, suna fuskantar matsananciyar matsalar rashin abinci. Hukumar bunkasa shiyyar arewa maso gabas ta NEDC ita ce ke da alhakin raba abinci ga ‘yan gudun hijiran a bayan kowanne wata uku.
Rahoton Voa Hausa ya labarto cewa; bincike ya nuna cewar ‘yan gudun hijiran sun shafe wa’adin da aka yi musu alkawari na za a rinka ba su abinci a kowanne wata uku, amma ba a ba su ba, duk kuwa da cewa an kawo kayan abincin har sun soma lalacewa.
Shugaban ‘yan gudun hijiran a jihar Bauchi, Buba Musa Shehu ya shaida wa wakilin muryar Amurka cewa, ‘yan gudun Hijirar suna cikin halin galabaita, ba sa samun abinci kuma an killace su an hana su fita su nemo abincin. Ya ce, kungiyar “North East Development, NEDC” ita ta ke kawo musu abinci, amma a yanzu ba sa samu.