Kakakin majalisar Tarayya, Benjamin Kalu, ya bayyana cewa ‘yan majalisar Tarayya sun talauce, shiyasa ba sa iya gudanar da ayyukan da ke kawukansu yadda ya kamata. Inda ya nemi a kara yawan kudaden da ake bai wa ‘yan majalisar.
Dan majalisar na jam’iyyar APC daga jihar Abiya wanda ya kuma kasance Kakakin majalisar, ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis, inda ya ci gaba da cewa; “na fada da farko, ina kara kuma jaddada, ba na kuma tsoron sake fada”, inji shi.
Sun kara da cewa; “wannan shi ne gaskiya, har sai ‘yan Nijeriya sun gane cewa kudaden da ake bai wa ‘yan majalisar wajen gudanar da majalisar a lokacin da Dala Daya take naira 180, yanzu ya yi kasa ma da yadda ake bayarwa a baya”, inji Kalu.