By Ishaq Dabai
Majalisar wakilai da sauran masu ruwa da tsaki sun yi watsi da kudirin dokar inganta Cibiyar Kula da Harkokin Kasa da Kasa ta Najeriya, NIA, zuwa cibiyar bayar da digiri.
Wannan yarjejeniyar tana zuwane a wani taron jin ra’ayin jama’a a Abuja da aka gudanar kan kudirin dokar daza ta soke da sake aiwatar da Cibiyar Harkokin Kasa da Kasa ta Najeriya (NIIA).
Kwamitin Majalisar Wakilai kan Harkokin Kasashen Waje, wanda dan majalisar wakilai Yakub Buba, na jam’iyar (APC-Adamawa) shine ya shirya taron jin ra’ayin jama’a.
Masu ruwa da tsaki a cikin abubuwan da suka gabatar, suna kara muryoyin su ga bukatar yin garambawul a kwalejin, Ministan Harkokin Waje, Mista Geoffrey Onyeama, ya yabawa kwamitin kan shiga tsakani.
Wakilin Amb.Daraktan ofishin babban sakatare a ma’aikatar, Onyeama yace hukumar ta NIIA wata hukuma ce a karkashin ma’aikatar wacce ke bada dama ga kasar don cika aikinta.
Osaghae yace kasafin kudin na shekarar 2021 da aka ware wa cibiyar Naira miliyan 46 ne kacal, inda ya bayyana dalilin faduwar darajar ta, A cewarsa, cibiyar tana da membobi 78 ne kawai, daga ciki tara ne, ciki har da babban darakta masu bincike ne.
Tun da farko, kakakin majalisar, majalisar wakilai Femi Gbajabiamila, ya nemi goyon bayan Majalisar Dokoki ta kasa a kokarin ta na sake fasalin wannan cibiya, majalisar ta cimma burinta.