Daga Abdullahi Kebbi.
‘Yan majalisar wakilan Amurka da suka hadar da ‘yan majalisu musulmai masu wakiltar Minasotta, Illahn Omar, da mai wakiltar Indiana Andre Carson, Dakuma mai wakiltar michigan Rashida Tlaid, sune suka shirya wannan buda baki a zauren majalisar kasar Amurka.
An shirya wannan taron buda bakin ne tare da sa hannun kungiyar Lauyoyi musulmai ta kasar Amurka, inda aka samu halartar yan majalisu da dama, dakuma wasu ma’aikatan majalisar dokokin kasar Amurka.
A wani jawabi da yar majalisa mai wakiltar Michigan tayi ta bayyana cewa ” wannan taro, taro ne mai matukar muhimmanci a tarihi ”
Wannan taro dai shine karo na farko wanda musulmai ke fatar ganin anci gaba dayin sa domin ta hakane addinin musulunci zai kara samun gindin zama a kasar Amurka.