Yan majalissun Arewa na tattaunawa don magance matsalar tsaro a yankin
Hon. Ysusf Ibrahim Zailani shugaban Yan majalissun Arewa sun gabatar da shawar wari don gani an kawo karshen rashin tsoro dake addabar yankin.
Ya bada bayani hakan ne lokacin da yake jawabin maraba a wani taro a Kaduna ranar Talata.
KARANTA:- Jami’ar Jos sun dauki Yan sakai don yin gadin Dalibai
A wani zancen da yafito ta mataima kinsa na kafar sada zumunta Ibrahim Dahiru Danfulani yanayin rashin tsaro dake addabar yankin abune na damuwa sosai da tashin hankali.
Kamar yadda yace hakan ya haddasa tsadar kayan abinci inda manoma na tsoron komawa gonakinsu saboda harkar rashin tsaro.
Dayawa daga cikin manoman na gudun kada su shiga gona a kwashe su ko a kashe su.
Sannan Zailani ya shawarci sauran dasu gaggawan ko wata mafita da zai kawo karshen rashin tsaro da talauci dake addabar yankin.
Daga karshe sunyi kira ga gwamnatin tarayya da agazawa Arewa da matakan tsaro musamman yanki Borno da wasu yankunan.