Gwamnatin Tarayya, a yau Laraba , ta karbi mutane 162 da suka dawo daga Libya. Inda Suka isa filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas da misalin karfe 2:10 na safe.
Jirgin dai ya taso ne daga birnin Tripoli na kasar Libya da misalin karfe 10:10 na daren ranar Talata.
Hukumar Kula da Masu gudun Hijira ta Duniya (IOM) ce ta ba su damar tafiya gida ta hanyar shirin komawa gida na kashin Kai, domin neman rage masu kwarara zuwa kasashen Turai daban-daban.
Wadanda aka dawo da su sun hada da mata 98, maza 28, yara mata 19, yara maza biyar, jarirai mata tara, da jarirai maza uku.
Daga cikin wadanda aka dawo da su har da wasu mutane biyar, wadanda ke da digiri a fannin kiwon lafiya.
Hukumomin da suka tarbi ‘yan gudun hijirar sun hada da sashin kula da lafiya na tashar jiragen ruwa na ma’aikatar lafiya ta tarayya, hukumar kula da ‘yan gudun hijira, Hukumar Bada Agajin gaggawa ta kasa NEMA, da kuma hukumar kula shige da fice ta Najeriya.