Akalla ‘yan Najeriya 500,000 ne za a dawo da su daga kasashen Libya, Mali, Chadi, Nijar, Kamaru da sauran kasashen duniya a shekarar 2022.
Shugaban hukumar kula da ‘yan gudun hijira da bakin haure da ‘yan gudun hijira ta kasa (NCFRI), Imaan Suleiman-Ibrahim, ne bayyana hakan a lokacin da ya bayyana a gaban kwamitin majalisar wakilai kan ‘yan gudun hijira a ranar Litinin domin kare kudirin kasafin kudin shekarar 2022.
A yayin gabatar da jawabinta ya bayyana cewa Najeriya za ta karbi bakuncin ‘yan gudun hijira kusan 73,000 daga kasashe 23 tare da ‘yan Najeriya sama da 500,000 da ke jiran dawo da su daga kasashen Chadi, Nijar, Kamaru, Mali, Libya da sauran kasashe.
Sai dai wani mamba a kwamitin Mai suna Darlington Nwokocha a lokacin da ya ke mayar da martani ga jawabin Shugaban hukumar ya ce, akwai bukatar hukumar ta bayar da cikakkun bayanai kan ‘yan gudun hijira da kuma kasashen da ake sa ran za su fito.
KARANTA WANNAN LABARIN: Zan Iya Lashe Zaben Anambra inji Dan Jam’Iyar PDP
Ya kuma ce akwai bukatar Hukumar ta yi karin bayani game da manyan ayyuka da hukumar ke shirin yi a shekarar 2022, inda ya ce; “Kudirin ku ba shi da cikakkun bayanai kuma ba shi da ma’ana don lissafin da ya dace.”