Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa kashi 63 cikin 100 na mutanen Najeriya miliyan 133 na fama da talauci.
An gabatar da wannan adadi ne yayin da ake kaddamar da bincike kan Talauci na Najeriya Multidimensional Poverty Index (MPI) a Abuja ranar Alhamis.
KARANTA WANNAN LABARIN: 2023: PDP Tace Tana Da Tabbacin Lashe Jihar Legas Da Wasu Jihohi 24
Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS), Ofishin Kula da Safety-Nets na kasa (NASSCO), Hukumar Bunkasa Ci Gaban Majalisar Dinkin Duniya (UNDP), Asusun tallafawa Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), da kuma Oxford Poverty and Human Development Initiative (OPHI) ne suka gudanar da shi.
Daily Trust ta rawaito cewa, matakin da aka yi amfani da shi wajen kididdige wannan adadi ya samo asali ne a kan MPI da ke da bangarori biyar na kiwon lafiya, da rayuwa, ilimi, tsaro da kuma rashin aikin yi.
Binciken wanda ya yi misali da gidaje sama da 56,000 a fadin Jihohi 36 na Tarayya da Babban Birnin Tarayya Abuja, wanda aka gudanar tsakanin watan Nuwambar shekarar 2021 zuwa Fabrairu 2022, ya nuna cewa kashi 65 cikin 100 na talakawa, miliyan 86, suna zaune ne a Arewa, yayin da kashi 35, kusan Miliyan 47 suna zaune a Kudu.
Ya bayyana jihar Sokoto a matsayin wacce tafi kowacce jiha yawan talauci a fadin Jihohin kasar, inda take da kashi 91 cikin dari yayin da Ondo ke da kaso 27 cikin dari.
Da yake jawabi a wajen taron, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce an dauki matakin ne domin ya samar da hanyoyin da za a iya gano talauci da kuma tinkarar manufofi.
Buhari ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan fadar sa Farfesa Ibrahim Gambari.
Rahoton ya kara da cewa, “sama da rabin al’ummar Najeriya talakawa ne masu yawan gaske kuma suna yin girki da itace ko gawayi, maimakon makamashi mai tsafta. Babban rashi kuma yana bayyana a cikin ƙasa a cikin tsafta, lokacin kiwon lafiya, rashin abinci, da gidaje. ”
“Gaba ɗaya, yawan talaucin kuɗi ya yi ƙasa da yawan talaucin da ake fama da shi a yawancin jihohi. A Najeriya, kashi 40.1% na mutane matalauta ne bisa ga tsarin talauci na kasa na shekarar 2018/19, kuma kashi 63% na fama da talauci da yawa a cewar MPI 2022.
Ma’aikatar Tattalin Arziki da Zamantakewa ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce yawan al’ummar Najeriya ya kai miliyan 216 a shekarar 2022, wanda ya kai kashi 2.7 cikin 100 na al’ummar duniya biliyan 8.
A WANI LABARIN KUMA: Kotu ta raba auren da ya Shekara 8 saboda rashin biyan haƙƙin Miji
Wata kotun Jos ta tsakiya da ke zamanta a Kasuwan Nama 1 a ranar Alhamis, ta raba auren shekara 8 da aka yi tsakanin wata Samira Makama da mijinta, Muhammed Musa, bisa rashin iya ciyar da iyalinsa.
Kwamitin alkalan da suka hada da Malam Sadiq Adam da Mr Hyacinth Dolnanan a wajen amincewa da bukatar da Makama ya gabatar, sun ce duk kokarin sasanta bangarorin ya ci tura.
Alkalan sun umarci mai kara da wanda ake kara da su bi hanyar Sasanci amma hakan bai haifar da ɗa mai ido ba.