Hukumar bada agaji ta gaggawa ta kasa wato NEMA, a ranar Talata ta karbi ‘yan Nijeriya 173 da suka dawo daga kasar Libya. Inda dawowarsu din ya biyo bayan zaman jangwam da firgici da suke yi a kasar bayan sun tafi fatauci daga Nijeriya.
‘yan Nijeriya sun sauka a filin jirgi na Murtala Muhammed dake Legas. Inda Alhaji Abubakar Muhammed Kodinetan NEMA din reshen Legas ya ce sun sauka ne a tawaga biyu ta sashen Cargo na filin jirgin.
Muhammed ya ce ‘yan Nijeriya sun dawo ne tare da taimakon hukumomin IOM, EU da kuma VRP wanda aka fara aikin taimakon da su tun cikin watan Afrilun 2017.