Wasu ‘yan kungiyar sakai a yankin Maza-Kuka a jihar Neja sun bayyana cewa, sun kashe Hakimin Adogon Malam Mai suna Alhaji Sa’idu Abubakar da Dan uwasa Alhaji Salihu Abubakar.
Kisan dai ya faru ne sa’o’i kadan bayan da wasu ‘yan bindiga suka kai hari a wani masallaci da ke Maza-kuka a karamar hukumar Mashegu da ke jihar, a lokacin sallar asuba (Subhi) inda suka kashe masu ibada 18, tare da sace wasu 13.
Wata majiya ta ce, ‘yan sakan sun kai farmaki garin Adogon Malam ne da misalin karfe 10 na safiyar ranar Litinin, inda suka kashe mutanen biyu bisa zargin cewa, suna da hannu a harin da aka kai da safiyar ranar Litinin.
Garin Adogon Malam dai makwabta ne da garin Maza Kuka da Yan bindiga suka farmaka
KARANTA WANNAN LABARIN: Yan bindiga sun kakkaba wa Al’umomin Sokoto Haraji
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Wasiu Abiodun, bai iya tabbatar da ko ramuwar gayya ce ba, amma ya ce, wani bangare ne na harin da aka kai a safiyar ranar Litinin.
A halin da ake ciki, Gwamnan Jihar Neja, Abubakar Sani Bello, ya roki gwamnatin tarayya da ta ba da umarnin tsawaita hare-haren da sojoji ke kai wa a jihar, domin dakile hare-haren da ake kai wa al’umma a jihar.
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake mayar da martani ga harin da aka kai wa masu ibada a ranar Litinin a garin Maza kuka.
Gwamnan, a cikin wata sanarwa da babbar sakatariyar yada labaransa, Mary Noel-Berje, ta fitar, ta ce, za a iya kawar da ‘yan bindiga gaba daya, kuma cikin kankanin lokaci, idan aka kai musu hari a lokaci guda.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa, tuni ya fara ganawa da shugabannin hukumomin tsaro a jihar, domin duba dabarunsu kan yadda za a dakile ayyukan ‘yan bindigar.