An kama tare da tsare Dattijon nan mai suna Abdullahi Ibrahim, mai shekaru 81, da dansa, Abubakar Ibrahim, wadanda suka yi zargin bacewar shanun su guda 31, a ofishin ‘yan sandan Jihar Kaduna.
An kama tsohon da dan na shi ne a ranar Talata, da misalin karfe 5 na yamma, a fadar dagacin Rigachikun.
Karamin Dan tsohon mai suna Abdulhamidu Ibrahim, ne ya shaidawa wakilinmu yanda aka kama Baban na shi da kuma dan’uwan shi, ya ce, an kama su ne a ranar Talata, a lokacin da wasu dattawan Anguwar suka gayyace su zuwa fadar dagacin domin a yi sasanci a kan yanda za a gano shanun.
“A lokacin da suke a can din ne, sai ‘yan sanda suka yi awon gaba da su, suka kuma tsare su. nan take sai aka kama su a kan dagewar da suka yi na sai sun gano inda shanun na su da suke hannun ‘yan sanda suka shiga, da kuma kan yanda suka shaidawa manema labarai faruwan lamarin,” kamar yanda ya yi zargi.
Ya ce, tun daga lokacin da Baban na shi da kuma dan’uwansa suka yi hira da manema labarai a kan batun bacewar shanun na su ne ake ta yi masu barazana.
Matashin, ya yi kira ga gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai da babban sufeton ‘yan sanda na kasa, da su kawo masu dauki su kuma kare su a kan uzzurawar da ake yi masu.
Da aka tuntubi Kakakin rundunar ‘yan sanda na Jihar Kaduna, DSP Yakubu Sabo, cewa ya yi, kamun ba shi da nasaba da maganan, amma dai zai yi bincike a kan wannan zargin, daga bisani ya ce zai kira wakilin namu domin ya yi masa bayani.
“Kamun ba shi da nasaba da maganan ta farko, amma zan yi kokari na binciko a kan wannan sabon zargin da ake yi, zan kira ka daga baya,” in ji shi.