Rundunar ‘yan sandan jihar Benue a ranar Litinin ta ankarar da mazauna jihar kan wani sabon tashin hankali da wasu da ba a San ko suwaye ba suka yi amfani da su, wajen kashe wadanda suka rasa rayukan su a jihar.
Wakilin Majiyar Jaridar Dimokuradiyya ya ruwaito cewa, sanarwar da rundunar ‘yan sandan ta yi, mai yiwuwa bai rasa nasaba da kisan wata budurwar da aka gano gawarta a ranar Lahadin da ta gabata, a kusa da tsohuwar gadar da ke kan hanyar zuwa bankin Arewa da ke unguwar Makurdi, babban birnin jihar.
Idan ba a manta ba a makwanni biyu da suka gabata irin wannan lamari ya faru inda aka gano gawar wata matashiya da ta kammala karatun digiri, kuma ta ke jiran takardar neman izinin fara yiwa kasa Hidima wato NYSC a cikin bankin arewacin kasar nan, bayan wani abokin cinikin bankin da ba a san ko wanene ba ya kira ta ta wayar tarho, domin tallafama ta.
KARANTA WANNAN LABARIN: INEC ta Sami Sabbin Masu Rajistan Katin Zabe
Comments 1