Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta kama wasu mutane 15 da ake zargi da yin garkuwa da mutane, satar shanu, fashi da makami da safarar mutane, tare da kwato shanu 500 a wasu samame daban-daban a jihar.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Monday Kuryas ne ya bayyana hakan, yayin da yake baje Kolin wadanda ake zargin a ranar Laraba a Minna, inda ya ce an kama 10 daga cikin wadanda ake zargin ne biyo bayan samun bayanan sirri da ke cewa ‘yan bindiga sun kai farmaki kauyen Sonfada, Lapai, tare da yin garkuwa da mutane biyu.
Kurya ya ce an kubutar da mutane biyu da aka yi garkuwa da su ba tare da sun ji rauni ba, yayin da aka kama mutum 10 a dajin dauke da shanu kusan 500, baburan Bajaj biyu, kudi Naira 270,000 da dai sauransu.
Ya Kuma kara da cewa, an kama wasu mutane biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da kuma wani mai safarar mutane a karamar hukumar Nasko Magama da ke jihar a ranar 11 ga watan Nuwamba.
KARANTA WANNAN LABARIN: An kama Mutane 4 da Ake Zargin Yan bindiga Ne A Sokoto
Wadanda ake zargin, Samaila Makeri Auna da Musa Umar, an ce sun amsa laifin da ake zarginsu da aikatawa na garkuwa da mutane.
Makeri ya kuma amsa laifin safarar matasa sama da 30 daga jihohin Kebi da Neja zuwa jihohin Kwara da Oyo.