‘
Rundunar ‘yan sanda a jihar Delta ta tabbatar da gano wani gidan Samar da jarirai a unguwar Okpanam da ke karamar hukumar Oshimili ta Arewa a jihar.
Kakakin rundunar ‘yan sandan, DSP Bright Edafe, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a garin Asaba, inda ya ce jami’an ‘yan sanda daga hukumar bincike ta jihar (SID) da suka far wa wurin, sun ceto wasu mata masu juna biyu guda uku.
“A bisa bayanai, a ranar 10 ga Yuli, 2022, da misalin karfe 7:30 na yamma, jami’an hukumar bincike na jihar sun kai farmaki a wata masana’anta da ke unguwar Okpanam, karamar hukumar Oshimili ta Arewa.
“Jami’an sun ceto mata masu juna biyu guda uku da wasu mutane biyu da ake zargi; An kama Promise Ejogu da Aruna Sulieman.
“Bayanan da ‘yan sanda suka tattara sun nuna cewa daya daga cikin wadanda ake zargin Promise Ejogu, dan uwa ne ga shugaban wata kungiyar .
Edafe ya ce “Kungiyar ta ci gaba da rike matan kuma tana sanya su cikin ayyukan jima’i don daukar ciki,” in ji Edafe.
Kakakin ‘yan sandan ya ce a halin yanzu wadanda ake zargin suna tsare yayin da ake kokarin cafke sauran ‘yan kungiyar. (NAN).
A wani labarin Kuma.
Kansilolin PDP sun koka kan yawaitar kashe-kashe a Kudancin Kaduna
Kansilolin Jam’iyyar PDP daga yankin Kudancin Kaduna sun koka kan yawaitar hare-hare akan Al’ummomin su da ƴan ta’adda suke cigaba da yi.
Wannan na zuwanm ne a yayinda Kansilolin suka yanke hukuncin cewa Ɗan Takarar Sanata a yankin na Shekarar 2023, Barister Sunday Marshall Katung yana da hadin yadda za tabbatar da samun tsaro a yankin.
Da yake jawabi a lokacin taron Manema Labaru a ranar Alhamis, Shugaban Ƙungiyar Kansilolin Hon. Obed Danjuma Gankon yace yankin Kudancin Kaduna, kamar sauran yankuna a Jahar, yana fama da matsalar ƴan Ta’adda.
“Wannan ƴan ta’addan sun tada al’ummatai, sun yiwa mata fyaɗe, sun kashe tare da sace mutane, ciki har da yara. Sun lalata Al’ummomi, sun yara ba tare da gidaje ba,” Inji shi.
Gankon wanda yana tare da dukkanin Kansilolin PDP da sauran masu ruwa da tsaki daga yankin Kaduna ta Kudu, yace sun amince Katung ya wakilce su a Shiyyar.