Hukumar ‘yan sandan jihar Rivers ta tabbatar da kama wata mata mai matsakaicin shekaru mai suna Chinyere da laifin sace yarinyar makwabtanta.
Al’amarin ya faru ne a ranar Talata da ta gabata a yankin D-Line dake Fatakwal.
Mai magana da yawun hukumar’yan sandan jihar Nnamdi Omoni ya shaidawa Jaridar the nation cewa an kama wasu mutane biyu dake da alaka da laifin.
https://dimokuradiyya.com.ng/yan-sanda-sun-kashe-masu-garkuwa-da-mutane-har-mutum-8-a-jihar-taraba-2/
Omoni yace masu laifin za a kaisu kotu domin yanke musu hukunci, ita kuma yarinyar an maida wajen iyayenta.
An bayyana cewa matar ta bawa yarinyar magani ne sannan daga bisani ta saka cikin wani akwati sannan ta nufi tashar mota domin guduwa da ita.
Jaridar the nation ta rawaito cewa mai lafin ta amsa cewa ta bawa yarinyar magani sannan kuma ta saka ta cikin akwati.
Yarinyar an fito da ita daga cikin akwatin sharkaf cikin gumi tana kuka.