Jami’an Rundunar yan sanda a Jigawa sun cafke wani mutum mai shekaru 25, bisa zargin shi da yin lalata da akuya a karamar hukumar Gwaram dake jihar.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan jihar Jigawa, ASP Lawan Shiisu ne, ya tabbatar da kamun wanda ake zargin, a cikin wata sanarwa da ya fitar a a garin Dutse Babban Birnin jihar a yau Juma’a.
Shiisu ya ce, jami’an Yan sanda sunyi nasaran kama wanda ake zargin ne, da misalin karfe 1 na safe, yayin da jami’an rundunar ke sintiri a cikin garin Gwaram.
Ya bayyana cewa wanda ake zargin, mazaunin unguwar Kunnadi ne, yayin da jami’an rundunar dake sintiri a yankin suka cafke shi, yana jima’i da Akuya.
KARANTA WANNAN LABARIN: Kotu ta umarci DSS ta biya Igboho Diyar Billiyan 20
“Da misalin karfe 0100 na safe, ‘yan sanda daga Shelkwatar Runduna ta Gwaram, yayin da suke sintiri a cikin garin Gwaram da kewayenta, sun cafke wani matashi dan shekara 25 mazaunin unguwar Kunnadi, yayin da yake saduwa da akuya,” inji Shiisu a cikin sanarwar.
Kazalika Kakakin ya kara da cewa, ana ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin, sannan idan an kammala za’a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu domin ya girbi abun da ya shuka.
A wani labarin Kuma na daban.
Rahotonni sun bayyana cewa a kashe wasu lauyoyi a jihar Imo da Darlington Chidume Odume, wanda aka fi sani da Omekagu.
Daya daga cikin Wanda abin ya rutsa da shi, wanda aka ce matar sa ‘yar sanda ce da ke aiki,matar tace ta samu labarin an kira shi zuwa Bar kimanin shekaru biyar da suka gabata.
Kisan nasa ya zo ne kwanaki biyu kacal bayan da aka kashe wani limamin cocin Anglican, Rabaran Emeka Merenu a gidan sa dake unguwar Iheteukwa, karamar hukumar Orsu, wanda har yanzu ba a san ko su wanene ba.
An bayyana cewa maharan sun harbi Odume ne a gaban wani babban kanti a Umudara Amaifeke Orlu, dake karamar hukumar Orlu ta jihar.
Wata majiya ta shaida wa manema labarai cewa Marigayin Odume mashahurin lauya ne a Orlu wanda ke kula da wasu kararrakin wadanda aka kama dangane da tashin hankalin da ya dabaibaye yankin.
A cewar majiyar, wanda abin ya rutsa da shi, tuni aka garzaya da shi zuwa asibiti a yankin amma aka ki karbarsa inda kuma aka tura shi zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jihar Imo, sai dai kuma Orlu, ya rasu a kan hanyar zuwa asibitin koyarwa, An jefa dukkan al’umma cikin makoki, “in ji majiyar.
Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan, CSP Michael Abattam, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce Kwamishinan‘ yan sandan, Hussaini Rabiu ya ba da umarnin yin cikakken bincike a kan lamarin dan cafke wadanda suke da hannun akan lamarin,” in jishi.
Comments 1