Akalla mutane 30 da aka yi garkuwa da su a karamar hukumar Toto ta jihar Nasarawa aka kubutar da su bayan wani samame da jami’an rundunar ‘yan sandan jihar tare da hadin gwiwar kungiyar ‘yan banga ta Miyetti Allah suka kai a yankin.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Ramhan Nansel, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Lafia ranar Juma’a.
KARANTA WANNAN LABARIN: Zan Cire Tallafin Man Fetur Idan Aka Zabe Ni Shugaban Kasa A 2023 – Tinubu
Ya ce, “A ranar 12 ga watan Janairu, 2023, an samu labarin cewa an ga wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a dajin Sardauna na karamar hukumar Toto, jihar Nasarawa inda suka yi garkuwa da wadanda abin ya shafa.
“Saboda wannan mummunan ci gaban, jami’an rundunar tare da hadin gwiwar kungiyar Miyetti Allah Vigilante na karamar hukumar Toto sun gudanar da aikin hadin gwiwa.
“Duk da haka masu garkuwa da mutanen sun bi sawun su a dajin Sardauna, kuma da ganin jami’an ‘yan sandan, sai suka tarwatsa cikin dajin cikin rudani.
“Saboda haka, mutane talatin (30) da aka yi garkuwa da su da suka hada da maza 20 da mata 10 an ceto su ba tare da sun ji rauni ba kuma an kai su asibiti domin duba lafiyarsu kuma za su sake haduwa da danginsu bayan an yi musu bayani.”
Nansel ya kara da cewa kwamishinan ‘yan sandan, Maiyaki Baba, ya yaba da jajircewar da jami’an ‘yan sanda da kungiyar ‘yan banga na Miyetti Allah suka yi domin gudanar da aiki mai kyau, sannan ya bayar da umarnin a ci gaba da toshe duk wani daji da dazuzzuka a fadin kananan hukumomin jihar 13.
A wani labarin kuma, Najeriya Ba Za Ta Iya Ci Gaba Da Karbar Bashi Ba —Lawan
Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan, ya bayyana cewa Majalisar Dokoki ta Tarayya za ta mayar da martani ga hukumomin samar da kudaden shiga daban-daban don samun isassun kudaden shiga don aiwatar da kasafin Naira tiriliyan N21.83tn na 2023.
Lawan ya bayyana haka ne a Abuja yayin bikin cikarsa shekaru 64 a duniya, inda ya jaddada cewa ba za a ci gaba da zama kamar yadda aka saba ba ga hukumomin samar da kudaden shiga na kasar nan, saboda gwamnati ba za ta iya ci gaba da karbar rancen kudi don gudanar da kasafin kudin ba.
Comments 1