Wasu jami’an ‘yan sanda sun afka wani guda bayan wani ya kira su yana shaida musu cewa an yi garkuwa da wani, Legit.ng ta ruwaito.
Yayin da ‘yan sandan su ka isa, sun ji hayaniya ta yi yawa inda su ka shiga da niyyar kai tallafi inda su ka gane ashe tsuntsu aku ne ke surutunsa.
KU KARANTA: 2023: Babban sifeton ‘yan sanda ya zargi gwamnati kan rikice-rikicen siyasa
Ana zargin mai tsuntsun ya koya masa surutun da yake yi wanda hakan ya janyo ‘yan sanda su ka isa wurin a rikice su na neman ba’asi.
Yadda tsuntsun ya dinga kuka yana neman taimako ne ya janyo hankalin ‘yan sanda inda su ka isa gidan da yake.
Kamar yadda bidiyon ya dinga yawo a Instagram, an samu rahoto kan yadda makwabcin wani mutum ya gayyaci ‘yan sanda bayan ya ji hayaniya ta yi yawa tamkar an yi garkuwa da wani mutum.
A bidiyon an ji inda Akun ya dinga rokon taimako yana bukatar a fitar da shi daga cikin kejin da aka sanya shi.
Yayin da ‘yan sanda su ka isa wurin, mutumin ya fito da akun wanda ya sanya wa suna Rambo.
A nan ne ya bayyana cewa tsuntsun ne ke ta surutu kuma su ka jin ma kansu. A bidiyon ne aka bayyana cewa ashe mutumin ne ya koya wa akun surutu.
Duk da haka akwai ma’abota amfani da Instagram din da su ka tambayi dalilin da ya hana jami’an bincike gabadaya gidan don sanin gaskiyar batun.
Za Mu Samar Da Ofisoshin ‘Yan Sanda Na Zamani A Fadin Kasar Nan – IGP
Babban Sufeto Janar na ‘yan sandan Kasar nan, IGP Usman Alkali Baba, ya yi alkawalin cewa za a kina ofisoshin ‘yan sanda na zamani irin wanda ‘yan sandan ke ginawa a fadin kasar nan.
Ya bayyana hakan ne a Ilorin, babban birnin jihar Kwara a ranar Talata yayin da yake kaddamar da daya daga cikin sabbin gine-gine na zamani a Madi, karamar hukumar Ilorin ta yamma.
Jaridar DIMOKURADIYYA ta rawaito cewa Da yake zantawa da manema labarai bayan kaddamar da aikin, IGP ya ce ginin zai kara kusantar da aikin ‘yan sanda ga jama’a.