Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Ogun sun kama wani matashi dan shekara 24 mai suna Mojiyagbe Olamilekan da laifin dabawa matarsa Mai suna Seun almakashi Kuma ta mutu har lahira.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi, ya shaidawa manema labarai a Abeokuta, babban birnin jihar cewa, an kama wanda ake zargin mazaunin Oke Ola a Ode Remo a karamar hukumar Remo ta Arewa a ranar Larabar da ta gabata. .
Ya ce kama shi ya biyo bayan kiran da ‘yan sanda suka samu dake cewa, wanda ake zargin ya kulle kansa da matarsa a dakinsu ya fara dukanta.
Ya bayyana cewa kukan matar ne ya jawo hankalin makwabta, inda suka yi kokarin shawo kan wanda ake zargin ya bude kofar, amma ya ki.
KARANTA WANNAN LABARIN: Sifeto Janar Ya Tura Sabon Kwamishinan Jihar Filato
“Bayan kiran wayan da aka yi ne, DPOn Ofishin Yan sanda dake Ode Remo Dibision, CSP Olayemi Fagbohun, ya tura jami’ansa suka nufi gidan mutumin, inda aka bude kofar gidan ma’auratan.
“An sami wacce aka kashe tana kwance a sume a cikin jini. Nan take aka kai ta asibitin jihar da ke Isara Remo inda likitan da ke bakin aiki ya tabbatar da rasuwar ta.” Inji shi.
“Ba tare da bata lokaci ba aka kama mijin kuma aka kai shi gidan yari, yayin da aka ajiye gawar wanda aka kashe a dakin ajiyar gawarwaki domin gudanar da Bincike,” in ji PPRO.
Ya Kuma kara da cewa, an mika wanda ake zargin ne bisa umarnin kwamishinan ‘yan sandan jihar, Lanre Bankole, zuwa sashin binciken kisan gilla na hukumar binciken manyan laifuka ta jihar, kuma za a gurfanar da shi bayan kammala gudanar da bincike.