Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta tabbatar da yin garkuwa da wani babban manajan hukumar tashar jiragen ruwa ta Najeriya, Mista Bashir Abdullahi mai shekaru 65 mai ritaya a gonarsa da ke dajin Barasa a karamar hukumar Sumaila ta jihar.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Haruna Abdullahi ya raba wa manema labarai a Kano yauAlhamis.
A cewar Abdullahi, “An tura tawagar ‘Operation Puff Adder’ domin ceto wanda aka sacr tare da cafke masu laifin.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “A ranar 03/11/2021 da misalin karfe 1630, an samu rahoton cewa, wasu mutane da ba a san ko su waye ba sun yi garkuwa da wani Bashir Abdullahi mai shekaru 65 a kauyen Sitti da ke karamar hukumar Sumaila a jihar Kano. a gonarsa, dake dajin Barasa na kauyen Gomo dake karamar hukumar Sumaila ta jihar Kano, mai iyaka da jihar Bauchi.
“Bayan samun rahoton, kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kano, CP Sama’ila Shu’aibu Dikko, ya tada tare da umurtar rundunar ‘Operation Puff Adder’ da su kubutar da wanda abin ya shafa, tare da kama masu laifin.”
Ya ce tun daga lokacin da rundunar ta fara aiki, binciken ya nuna cewa wanda aka ksace, ya koma yankin da gonar take ne na tsawon makonni biyu kafin Yan bindigan suyi Garkuwa da Shi.