By Abbas Yakubu Yaura
Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Kwara da sauran jami’an tsaro sun bazama zuwa dazuzzuka daban-daban a jihar Kwara domin neman Mista Mohammed Zarma, mataimakin Kwanturolan Hukumar Kwastam ta Najeriya mai ritaya, wanda aka yi garkuwa da shi a gonarsa da ke unguwar Egbejila a karamar hukumar Asa ta jihar a yammacin ranar Alhamis.
Mohammed, a cewar SP Ajayi Okasanmi, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar a ranar Alhamis yace da misalin karfe 5:30 na yammacin ranar Alhamis ake zargin an yi garkuwa dashi, a cikin gonarsa dake Oke Jia kusa da Egbejila da wasu ‘yan bindiga da ke magana da wani yare na Najeriya.
Rundunar ‘yan sandan ta ce ‘yan bindigar sun yi harbin bindiga a lokacin da suka yi garkuwa da kwanturolan kwastam mai ritaya, yayin da jami’an tsaro da suka ziyarci gonar suka samu nasarar kwato harsashi guda hudu da babu komai a cikin su.
Okasanmi a cikin wata sanarwa mai taken, ‘muna kokarin kubutar da wani da aka yi garkuwa da shi a gonar Oke Jia da ke yankin Egbejila a ranar Juma’a, ya ce, “Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara a karkashin jagorancin CP Tuesday Assayomo ta aike da jami’an ta da sauran kayan aikin da suka dace na mutane, sannan yace wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wani Mohammed Zarma ‘M’, mataimakin Kwanturola na Hukumar Kwastam ta Najeriya, wanda aka yi garkuwa da shi a gonarsa da ke Oke Jia, Egbejila da misalin karfe 17: 30 na ranar 6/1/2022.
“A ziyarar da jami’an rundunar suka kai wurin da lamarin ya faru, an kwato harsashi guda hudu da babu komai a ciki.
“Kwamishanan ‘yan sanda na jihar Kwara, CP Tuesday Assayomo, na fatan tabbatar wa iyalan wanda aka sace da kuma sauran jama’a cewa ba za a yi kasa a gwiwa ba wajen ganin an ceto wanda abin ya shafa tare da samun damar kama wadanda suka aikata laifin don Allah.” A cewar sanarwar.
A halin da ake ciki kuma jami’an tsaro na ci gaba da tona dazuzzuka a jihohin Kwara da Ekiti domin neman uku daga cikin hudun da aka sace, wadanda wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka yi garkuwa da su ranar Alhamis a hanyar Obo Ayegunle/Osi a karamar hukumar Ekiti ta jihar Kwara.
Wani makaniki mai suna Sunday Balogun, da matarsa mai juna biyu, Mary, sai almajirinsa, Taiye; An dai yi zargin an yi garkuwa da dan uwansa tagwaye, Kehinde a cikin wata mota kirar Toyota Sienna.
An ce wadanda lamarin ya rutsa da su na tafiya ne daga Obbo Ayegunle zuwa Osi a lokacin da masu garkuwa da mutane suka yi garkuwa da motarsu a tsakiyar hanyar mai tsawon kilomita 12.
Wani jami’in tsaro da bai so a ambaci sunansa ba ya ce wata mata mai suna Mary da ake kyautata zaton matar makanikin ce ta samu nasarar kubutar daga dajin da hadin gwiwar jami’an tsaro da aka tura domin ceto wadanda lamarin ya shafa.
Wata majiya ta kusa da dangin da ta so a sakaya sunanta, ta ce masu garkuwa da mutanen sun tuntubi iyalan, inda suka bukaci a biya su naira miliyan 10m.
“Sun tuntubi ‘yan uwa suna neman a biya su Naira miliyan 10m. Mun samu damar tattaunawa akan naira miliyan 4m. Duk da cewa ‘yan uwa da al’umma sun samu damar tara Naira miliyan 2m; sun yi watsi da hakan kuma sun ba da umarnin a sayar da wata motar bas Toyota Sienna a cikin bitarsa don biyan kudin fansa,” inji shi.
Jami’in tsaron ya shaida wa wakilinmu cewa, an tura jami’an tsaro daga dukkan hukumomin tsaro da mafarauta da kungiyoyin sa-kai don bin diddigin wadanda suka sace tare da neman sauran ukun da aka sace a dazuzzukan jihohin Kwara da Ekiti.