By Abbas Yakubu Yaura
Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kashe ‘yan sanda uku da wani direban babur a garin Suleja na jihar Neja.
Jaridar Daily Trust ta tattaro cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 11 na daren ranar Alhamis.
Indiya: Wasu Iyaye Sun Shigar Da Karar Dan Su Da Matar Sa Kan Rashin Haifo Musu Jika
Rahotanni sun ce ‘yan sandan na amsa kiran gaggawa ne a lokacin da aka yi musu kwanton bauna a kusa da wani wuri da ake kira Old Barracks.
Wata majiya ta ce “‘yan bindigar sun yi musu kwanton bauna, wadanda da alama suna tsammanin isowarsu ne don su far musu da harbi.”
Shugaban karamar hukumar Suleja, Abdullahi Shuaibu Maje, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce kimanin mutane uku ne suka tsira daga harin, ciki har da dan banga.
Sannan ya ce yanzu haka Wadanda abun ya shafa suna jinya a wani asibiti da ke yankin.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Wasiu Abiodun, bai amsa kiran waya ba ko kuma amsa sakon da aka aika masa har zuwa lokacin hada rahoton.