Rahotanni sun bayyana yadda ‘yan sanda sun yi nasarar ceto wasu dakarun Soji 2 daga hannun kungiyar Boko Haram a Maiduguri da ke jihar Borno mai fama da ayyukan ta’addanci.
Gidan Rediyon Faransa ya labarto cewa; wasu bayanai da shafukan yada labaran kasar suka wallafa sun ce mayakan na Boko Haram sun yi garkuwa da Sojin ne a wani farmaki da suka kai ranar 13 ga watan nan kan dakarun da ke rangadi akan titin Auno tare da hallaka 2 baya ga garkuwa da wasunsu.
Acewar bayanan an samu arangama tsakanin Jami’an ‘yansandan da mayakan kungiyar ta’addanci da ya kai ga kashe da dama baya ga kwace wasu makamai da kuma ceto Sojin biyu.
Ko a litinin din da ta gabata sai da Sojin Najeriya suka fatattaki mayakan na Boko Haram a wani makamancin farmakin da ke kokarinsu na kwace iko da wani barikin Soji da bai yi nasara ba.
Bayanan sun nuna cewa a wancan farmakin an yi artabun da ya kai ga rasa rayukan Sojin Najeriyar da dama.