Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso ya bukaci ‘yan siyasa su gina jama’a maimakon sace dukiyar al’umma.
Kwankwaso ya yi wannan tsokaci ne a Minna a ranar Alhamis a lokacin da ya zama shugaba a wajen taron kaddamar da zababben gwamnan jihar Neja, Mohammed Bago.
KU KARANTA: Ban San Komai Ba Game Da Ma’aikatar Ilmi Sanda Aka Nada Ni Minista – Adamu
“Kudi ba shine duk abin da ya kamata a yi niyya don inganta rayuwar mabukata da wadanda aka zalunta ba”.
“Idan kana son sayar da gidaje, da gine-ginen jama’a, da sayar da majami’u ko masallatai ga abokanka da danginka, bayan ka bar ofis, za ka yi nadama,” in ji Kwankwaso.
Tsohon gwamnan ya bukaci zababben gwamnan da ya zuba jari mai tsoka a fannin ilimi da tsaro domin amfanin jihar Neja, ko kuma zai yi nadama a nan gaba.
Ya kara da cewa jarin da ake zubawa a fannin ilimi na iya yiwuwa ba lallai aga alfanunsa ba a nan take, amma a karshe zai haifar da sakamako mai kyau.
Ya kara da cewa idan Bago ya zama gwamna mai taka rawar gani, sai ya taka rawa nan take bayan an rantsar da shi kan ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin jihar.
Ya bayyana cewa rashin iya aiki da ilimi ya sa gwamnoni da dama da ba su da wani abin a zo a gani a jahohinsu bayan shekaru hudu ko takwas na mulki.
Tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa Farfesa Attahiru Mohammed Jega, wanda ya gabatar da muhimmin jawabi ya bayyana cewa, ya kamata a yi shugabanci nagari da shugabanni masu son kai da hangen nesa don magance bukatu da muradun al’umma.
Jega ya kuma bayyana cewa rashin shugabanci ne ke haddasa tabarbarewar tattalin arzikin da ake fama da shi a kasar nan inda ya kara da cewa akwai bukatar ma’aikatan gwamnati su kasance masu gaskiya da rikon amana a kowani lokaci.
A nasa jawabin, zababben gwamnan jihar Neja, Mohammed Bago, ya yi alkawarin zarce nasarorin da gwamnonin da suka Gabace shi suka samu a matsayin ma’auni wajen auna gwamnatocin da suka yi nasara a Arewa.
A wani labarin kuma: Kwanaki 5 Yabar Ofis: Buhari Ya Nada Sabon Shugaban Asusun Bunkasa Noma Na Kasa
Kwanaki biyar kafin barinsa ofis shugaba Buhari yayi wani sabon nadi.
Shugaba Buhari ya amince da nadin Garzali Muhammed Abubakar a matsayin babban sakataren asusun bunkasa noma na kasa.
Buhari ya nada akalla mutane bakwai a ofishin shugaban da mambobin kwamitin kungiyar.