Wadansu ‘yan siyasa na amfani da rashin tsaro a wasu sassan kasarnan domin cimma manufofinsu na kashin kasu, inji gwamnan Bello Matawalle na jihar Zamfara.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a ziyarar da ya kai a sansanin sojoji na ‘Super Camp 4’ dake garin Faskari a jihar Katsina, inda gwamnan ya ce wadanda suke kara rura wutar matsalar tsaro a kasarnan, ba su damu da jindadi da walwalar al’umma ba.
“Mu ‘yan siyasa, muke da alhakin matsalar tsaron nan da ya addabi al’ummarmu. A bayyane yake cewa wadansu ‘yan siyasa na amfani da matsalar tsaron nan domin cimma burinsu na siyasa. Wadannan baragurbin ‘yan siyasan zai yi wuya ka ji suna jinjinawa sojoji bisa nasarar da suke samu a fagen yakin da suke yi.” Ya tabbatar.
Har wala yau ya ci gaba da cewa; “A maimaikon haka ma har sauri suke su je kafafen watsa labarai su kai rahoton yadda ‘yan bindiga da wadansu batagari suka kai hare-hare.” Inji shi.
Gwamnan ya ce a wurin irin wadannan ‘yan siyasar, siyasa karbar mulki ne kawai, ba wai hidimtawa al’umma ba.
Gwamnan ya ce: “da wannan nake karfafa hukumomin tsaronmu cewa su yi maganin duk wanda yake kokarin siyasantar da tsaron kasarnan ko min girmansa. Da haka ne zamu iya magance matsalolin tsaron da yake addabarmu a yanzu ba kawai a arewa maso yamma ba, a kafatanin kasar ma baki daya.” Inji shi.
Gwamnan ya kai ziyarar ne da gwamnan Sakkwato, Aminu Tambuwal, da kuma Sanata Ali Ndume domin ganin irin shirin da sojojin suke da shi wajen kawo karshen matsalar.