Ma’aikata 23 na Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, a Jihar Kwara, na jiran hukunci kan samunsu da hannu wajen yin rajistar masu kada kuri’a ba bisa ka’ida ba a Jihar. Kamar yadda Daily Post ta ruwaito
Kwamishinan Zabe a INEC, Garba Attahiru Madami ne ya bayyana hakan a Ilorin a wani taron masu ruwa da tsaki da jam’iyyun siyasa masu rijista da zasu fafata a zaben 2023.
KARANTA WANNAN LABARIN: El-Rufai Ya Yabawa Sojoji Bisa Hallaka Jagoran Yan ta’adda
Ya ce adadin masu kada kuri’a a jihar Kwara a yanzu ya kai miliyan 1.6.
Ya yi Allah-wadai da yadda al’ummar Jihar ke ke tafiyar wahainiya wajan karbar katin zabensu na dindindin, inda ya ce daga shekarar 2011 zuwa 2019 hukumar ta na da adadin katunan zabe 233,856 da ba a karba ba.
Madami ya bayyana cewa a cikin adadin katunan zabe da ba a karba ba, 20,752 ne kawai aka karba a watan Oktoban 2022, yayin da sama da 193,000 suka rage ba a karba ba.
Ya bayyana cewa taron masu ruwa da tsaki ya zama wajibi a matsayin matakin farko na tabbatar da zabe mai cike da gaske da adalci a jihar a shekara mai zuwa.
Madami ya sha alwashin kare tsarin zabe ta hanyar gudanar da zaben gaskiya, da adalaci ta haryar lumana wanda zai zama abun alfarin mutanen Kwara.
A nasa jawabin, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Paul Odama, ya gargadi ‘yan siyasa game da sayen kuri’u da dokar zabe ta yi gargadi akan shi.
Ya kuma shawarce su da su shiga yakin neman zabe, su guji ‘yan daba da lalata allunan tallan jam’iyyun siyasa masu adawa da su.
Odama ya kuma gargadi ‘yan siyasa da su daina bai wa magoya bayansu miyagun kwayoyi domin tabbatar da yakin neman zabe da zabuka a jihar lami lafiya.
A WANI LABARIN KUMA: Da Dumi-Dumi: Ten Hag Ya Yanke Shawarar Saida Maguire
Kocin Manchester United, Erik ten Hag, zai nemi siyar da Harry Maguire a bazara mai zuwa yayin da yake ci gaba da sake gina kungiyar.
A cewar The Guardian, United za ta yi la’akari da tayin da za ta yi wa kyaftin din na ta, a wani yunkuri na tara kudin siyan wasu yan wasan.