A daidai lokacin da ake ci gaba da murnar ranar dimokuradiyya ta Najeriya, jami’ai da ma masu rike da madafun iko na ci gaba da kira da a tashi tsaye don ganin an shawo kan matsaloli dake addabar ƙasar.
Daga cikin masu wannan kira har da Sanatan mazabar Kaduna ta tsakiya a majalisar datijjai Sanata Uba Sani, inda ya ce tsarin mulkin dimokuradiyya a Najeriya ya kasance mai tsarkakiya, don haka tilas sai an haɗa hannun wajen ganin an inganta shi.
Yayin da yake taya yan Najeriya murnar ranar ta dimokuradiyya, Uba Sani ya yi ikirarin cewa jarumai da dama a kasarnan sun sadaukar da rayukansu da zummar alkinta rayuwar yan baya, don haka babu ta yadda kuma za a bari wasu tsiraru su wargaza kasar a tsari irin na dimokuradiyya.
“Dole ne a rana irin ta yau mu tuna da yan gwagwarmaya da suka sadaukar da rayukansu don ceto yan baya, irin su Marigayi Cif Ghani Fawehinmi (SAN, GCON) da Cif MKO Abiola (GCFR) da Dakta Beko Ransome Kuti gami da Chima Ubani.
“Hakika sun yi gwagwarmaya matuka ga mulkin kama karya na soji. Sun jagoranci masu fafutuka na farar hula da sauran masu kishin kasa don alkinta dimokuradiyya. Kuma duk sun yi hakan ne da niyyar samun jin dadi da walwalar mu” cewar Uba Sani.
Daga nan Uba Sani ya ja hankalin shugabanni da su yi karatun ta nutsu don su ma su bi sahun gwaraza da za a rika tunawa ko bayan ba sa nan.
Da ya tabo ɓangaren tsaro, Uba Sani ya bukaci yan kasa da su tashi tsaye su bada gudunmawarsu wajen ganin an shawo kan matsalar zubar da jini da ake ci gaba da yi a sassan Kasarnan.
Ya ce yanzu ya ce lokaci ya yi da za a baiwa matasa dama a ƙasarnan su gwada irin basirar fa Allah Ya musu.