No Result
View All Result
  • Login
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Kasashen Ketare
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
CONTACT US
SUBSCRIBE
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Kasashen Ketare
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
No Result
View All Result
Home Siyasa

Yanzu-yanzu: 2023: Peter Obi Ya Koma Jam’iyyar Labour, Ya Bayyana Dalilan Sa

Tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi ya koma jam'iyyar Labour Party.

Abbas Yakubu Yaura by Abbas Yakubu Yaura
May 27, 2022
in Siyasa
Reading Time: 2 mins read
0 0
0
Yanzu-yanzu: 2023: Peter Obi Ya Koma Jam’iyyar Labour, Ya Bayyana Dalilan Sa

By Abbas Yakubu Yaura

RELATED POSTS

Gwamna Ganduje Yace Tinubu Ba Dan Takara Bane Na Gwaji

Gwamna Ganduje Yace Tinubu Ba Dan Takara Bane Na Gwaji

July 2, 2022
2023: Buhari ya rantsar da Sabbin Kwamishinonin Hukumar INEC guda 6

INEC ta koka kan ƙarancin masu rajistar Katin Zaɓe a Jahar Katsina

July 2, 2022
Dalilin Da Yasa Nake So Na Zama Shugaban Kasa A Shekarar 2023, Al-Mustapha Ya Bayyana

Dalilin Da Yasa Nake So Na Zama Shugaban Kasa A Shekarar 2023, Al-Mustapha Ya Bayyana

July 2, 2022
Tinubu Ya Yi Biris Da Ni Bayan Na Janyewa Osinbajo A Zaben Fidda Gwani  – Dan Takara

Tinubu Ya Yi Biris Da Ni Bayan Na Janyewa Osinbajo A Zaben Fidda Gwani – Dan Takara

July 2, 2022
Rikicin PDP: Dalilin Da Ya Sa Gwamna Wike Ya Kusa Samun Bugun Zuciya — Kola Ologbondiyan

Rikicin PDP: Dalilin Da Ya Sa Gwamna Wike Ya Kusa Samun Bugun Zuciya — Kola Ologbondiyan

July 1, 2022
Majalisar Wakilai

Ƴan Majalisu sun buƙaci ƙarin shekarun aiki ga masu buƙata ta musamman daga 65, 70

July 1, 2022

 

Tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi ya koma jam’iyyar Labour Party.

Obi ya tabbatar da hakan ne a shafinsa na Twitter a ranar Juma’a yayin da ya yi rajista da jam’iyyar a gundumarsa ta Agulu dake jihar Anambra.

Da yake bayar da dalilan shiga jam’iyyar Labour, Obi ya ce: “Tunda na fice daga PDP saboda al’amuran da suka ci karo da mutuntaka da ka’idata, na tuntubi bangarori daban-daban da kuma wasu mutane domin ganin ba mu kawo cikas ga hanyar da za mu bi wacce ba ta dace da wurin da ake so ba.

“A gare ni, tsarin cimma burinmu yana da mahimmanci kamar abin da mutum zai yi bayan haka.

“Saboda haka, na zabi hanyar da nake ganin ta dace da burinmu na daga cigaban kasar nan.

Buy JNews
ADVERTISEMENT

“kuma ita ce jam’iyyar Labour wadda ta yi daidai da jama’a, ma’aikata, ci gaba, samarwa, tabbatarwa da kuma hada kan ‘yan Najeriya a matsayin iyali daya.

“Ina gayyatar duk ‘yan Najeriya da su zo tare da ni wajen kwato kasarmu.

“Ka tabbata cewa ba zan taɓa barin ka ba.”

Idan dai za’a iya tunawa a ranar 25 ga watan Mayu Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito tsohon Gwamnan Jihar Anambra Peter Obi ya bayyana janyewar sa daga neman takarar shugabancin Najeriya a karkashin Jam’iyyar PDP da kuma ficewa daga cikin ta kasa da sa’oi 72 kafin gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyar.

Rahotanni sun bayyana cewa Obi wanda ya marawa Atiku Abubakar baya a zaben shekarar 2019 ya rubuta wasikar ficewar sa daga Jam’iyyar ne ga shugaban ta Iyorchia Ayu ba tare da gabatar da dalilan daukar wannan mataki ba.

Wasikar ta bayyana cewar Obi ya gabatar da aniyar sa ta janyewa daga PDP kamar yadda doka ta tanada inda ya shaidawa shugaban mazabar sa dake Agulu ta 2 a Anaocha ta Jihar Anambra daga ranar 20 ga watan Mayu, matakin da ya kawo karshen aniyar sa ta tsayawa takarar shugaban kasa a Jam’iyyar.

Tsohon gwamnan wanda ya bayyana aniyar sa ta bada gudumawa wajen gina kasa, yace halin da ake ciki yanzu ba zai bashi damar yin haka ba ta hanyar da ta dace, duk da yake babu abinda ya sauya a shirin sa na bada gudumawa wajen ceto Najeriya.

Sai dai Daraktan yakin neman zaben sa Doyin Okupe ya tabbatar da cewar Obi zai tsaya takaran zabe mai zuwa ba tare da bayyana jam’iyyar da zai koma ba.

Tags: Jam'iyyar LabourPeter Obi
ShareTweetShare
Abbas Yakubu Yaura

Abbas Yakubu Yaura

Related Posts

Gwamna Ganduje Yace Tinubu Ba Dan Takara Bane Na Gwaji
Labarai

Gwamna Ganduje Yace Tinubu Ba Dan Takara Bane Na Gwaji

July 2, 2022
2023: Buhari ya rantsar da Sabbin Kwamishinonin Hukumar INEC guda 6
Labarai

INEC ta koka kan ƙarancin masu rajistar Katin Zaɓe a Jahar Katsina

July 2, 2022
Dalilin Da Yasa Nake So Na Zama Shugaban Kasa A Shekarar 2023, Al-Mustapha Ya Bayyana
Labarai

Dalilin Da Yasa Nake So Na Zama Shugaban Kasa A Shekarar 2023, Al-Mustapha Ya Bayyana

July 2, 2022
Tinubu Ya Yi Biris Da Ni Bayan Na Janyewa Osinbajo A Zaben Fidda Gwani  – Dan Takara
Siyasa

Tinubu Ya Yi Biris Da Ni Bayan Na Janyewa Osinbajo A Zaben Fidda Gwani – Dan Takara

July 2, 2022
Rikicin PDP: Dalilin Da Ya Sa Gwamna Wike Ya Kusa Samun Bugun Zuciya — Kola Ologbondiyan
Siyasa

Rikicin PDP: Dalilin Da Ya Sa Gwamna Wike Ya Kusa Samun Bugun Zuciya — Kola Ologbondiyan

July 1, 2022
Majalisar Wakilai
Labarai

Ƴan Majalisu sun buƙaci ƙarin shekarun aiki ga masu buƙata ta musamman daga 65, 70

July 1, 2022
Next Post
Ba Dole Bane Dan Takara Sai Ya Gabatar da Shaidar Biyan Haraji – INEC

Jam'iyyu Sun Saka INEC A Gaba, Suna Bukatar Karin Wa'adi

Ma’aikatan Kamfanin Simintin Dangote 3 Sun Mutu A Hadarin Mota, Da Dama Sun Jikkata A Kogi

Ma’aikatan Kamfanin Simintin Dangote 3 Sun Mutu A Hadarin Mota, Da Dama Sun Jikkata A Kogi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Choose A Language Here

Arabic Arabic English English French French Hausa Hausa

Siyasa

  • All
  • Siyasa
‘Yan Sanda Sun Harba Hayaki Mai Sa Hawaye Kan Masu Zanga-zangar A Dawa Da Gwamnatin  Burkina Faso

‘Yan Sanda Sun Harba Hayaki Mai Sa Hawaye Kan Masu Zanga-zangar A Dawa Da Gwamnatin Burkina Faso

November 27, 2021

Hanya Ɗaya Ce Kesa Jarumi Ya Kafa Kansa A Bollywood – Sachin Khedekar

October 1, 2020
Google

Bikin Ranar Mata Ta Duniya: Google zai tallafa wa mata masu sana’o’i da Dala Miliyan 1

March 8, 2022

Facebook

Twitter

Labarai

  • Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    27 shares
    Share 11 Tweet 7
  • Yan sanda a Katsina sun cafke yaro dan shekara 13 saboda ya kashe yan ta’adda

    14 shares
    Share 6 Tweet 4
  • Abuja: Musa Ɗan Shekara 16 shiya koya man neman Maza — Cewar Matashi Mai shekaru 36

    697 shares
    Share 279 Tweet 174
  • Yadda na rinka lalata da yar shekaru 32, cewar dan shekaru 13

    40 shares
    Share 16 Tweet 10
  • Asibitin Usman Danfodiyo ya dakatar da ma’aikaciyar da ta caccaka wa jaririya allura

    6 shares
    Share 2 Tweet 2
Dimokuradiyya

An Kafa Jaridar Dimokuradiyya Ne Domin Tabbatar da mulkin da Jama'a suka zaɓa da Kansu Domin su Amfana.

Recent Posts

  • Da Dumi-Dumi: Kungiyar NUJ ta Zamfara ta zabi sabbin shugabanni
  • Osibanjo Zai Wakilci Buhari a Taron ECOWAS karo na 61 a Ghana
  • Biles, Denzel Washington, Da Steve Jobs Daga cikin Masu Nasara Na Babbar Daraja Na Amurka

Quick Links

  • Tsaro
  • Siyasa
  • Labarai
  • Wasanni
  • Kasuwanci
  • Rikicin Duniya

Contact Us

info@dimokuradiyya.com.ng

0809 912 4425 +234 809 912 4425

No. 218 Mogadishu layout Kaduna City Center Ahmadu Bello way kaduna. Kaduna, Nigeria 800273

© 2021 Dimokuradiyya Media Services LTD - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Kasashen Ketare
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • Kiwon Lafiya
  • Ilimi
  • Kasuwanci
  • Noma Da Kiwo
  • Talla
  • Masarautu
  • Babu Maraya
  • Addini
  • Wa’azin Kirista
  • Girke-Girke
  • Waiwaye
  • Marubutanmu
  • Wasiku
  • Ni’ima Dai Mata
  • Bidiyo
  • Hotuna
  • Mujalla
  • Shirye-Shirye Na Musamman
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Yan Fim da Finafinai
  • Zauren Dimokuradiyya

© 2021 Dimokuradiyya Media Services LTD - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In