An yi wa Gwamna Samuel Ortom na Jihar Binuwai wata karamar tiyata.
Mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Terver Akase ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Larabar nan.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa a ‘yan kwanakin da suka gabata kafafen sada zumunta sun yi yada rashin lafiyar Ortom sakamakon hotunan filastar bandeji a kansa.
Wasu ‘yan jihar sun bukaci a yi bayani don share shakkunsu game da jita-jitar da ake yadawa kan lafiyar gwamnan.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Da yake mayar da martani, Akase ya ce ya zama dole a yi watsi da irin wadannan jita-jita domin ya bayyana cewa rashin lafiyar gwamnan ba wani abin damuwa ba ne.
“Mutane da dama sun yi tambayoyi game da filastar da ke goshin Gwamna Samuel Ortom a ‘yan kwanakin nan.
KARANTA KUMA: Gwamna Ortom Ya Musanta Rade-radin Da Ake Yi Tsakaninsa Da Atiku
“A matsayinsa na Gwamna wanda lafiyarsa ta shafi al’ummarsa, ya dace mu rika sanar da al’ummar Benue a kodayaushe game da ayyukansa, lafiyarsa da motsinsa.
“Kamar kowane dan Adam, Gwamna Ortom ya samu rauni a gefen goshinsa na dama kuma an yi masa wata karamar tiyata. An sanya filastar don hana kamuwa da wata cuta. Ba wani abu ba ne mai tsanani ka da a damu.
“Muna matukar godiya da duk kiraye-kiraye da tambayoyi daga mutanen kirki na jihar Binuwai. Gwamna Ortom na cikin koshin lafiya kuma ya ci gaba da gudanar da ayyukan sa, daya daga cikin ayyukan yau da kullum na hukumar Aper-Aku Lodge da aka sake ginawa tare da inganta shi a cikin jama’ar Benue, Makurdi ta Ag. Shugaban BOT, jam’iyyar PDP, Sanata Adolphus Wabara,” inji Akase.
A wani labarin kuma: Rikicin PDP Ya Kara Ta’azzara Yayin Da Magoya Bayan Wike Suka Janye Jikinsu
Magoya bayan Gwamna Nyesom Wike na jihar Ribas sun fice daga kwamitin yakin neman zaben Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake cigaba matsin lamba ga Shugaban Jam’iyyar na kasa, Sanata Iyorchia Ayu da ya sauka daga mukamin.