An sallami mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo daga asibiti sakamakon samun nasarar yi masa tiyata da gyaran jiki.
Mataimakin shugaban kasar ya shafe kwanaki 7 a asibitin Duchess na Legas tun ranar 16 ga watan Yuli, inda aka yi masa aurin karaya.
Babban Likita na Mataimakin Shugaban Kasa, Dr Nicholas Audifferen, ya bayyana hakan a ranar Litinin cewa aikin da akayi wa magaimakin shugaban nasa ya yi nasara “ba tare da wata matsala ba.”
“An kwantar da Mataimakin Shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo, SAN a Asibitin Duchess International Hospital, dake jihar Legas, a ranar Asabar da ta gabata, 16 ga Yulin shekarar 2022, saboda karayar da ya samu. Kuma An yi masa tiyatar gyara ba tare da wata matsala ba.”
“An kwantar da shi tsawon kwanaki 7 a lokacin tiyatar. bayan tiyatar da aka yi masa. An sallame shi kuma yanzu yana samun sauki,” inji shi.
Ya kara da cewa mataimakin shugaban kasar ya mika godiyar sa ga ma’aikatan asibitin bisa irin kulawar da suka yi masa tare da aiki cikin nuna kwarewa da inganci, sannan ya yaba da fatan alherin da shugaban kasa Buhari ke yi da kuma duk wadanda suka aiko masa da sakon fatan alheri.
Ya ce, “Farfesa Osinbajo yana godiya ga daukacin ma’aikatan asibitin karkashin jagorancin babban jami’in gudanarwa, Dokta Tokunbo Shitta-Bey da Daraktan Likitoci, Dokta Adedoyin Dosunmu-Ogunbi bisa kwarewa da ingancin kulawa da suka nuna.
“Mataimakin shugaban kasar ya kuma yaba tare da fatan alherin shugaban kasa Muhammadu Buhari, ‘yan Najeriya daga kowane bangare na rayuwa da kuma kowa da kowa a gida da waje domin fatan alheri.
“Mataimakin Shugaban kasan zai ci gaba da murmurewa a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa.”
A wani labarin kuma na daban.
Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da wasu ma’aurata biyu a kauyen Sheda da ke karamar hukumar Kwali a Abuja.
Wani dan uwan ma’auratan da ke zaune a Goni Gora Kaduna, Alih Moses ya shaidawa Jaridar DAILY POST, a ranar Litinin, cewa an yi garkuwa da kaninsa, Mista Sunday Odoma Ojarume da matarsa Mrs Janet Odoma Ojarume daga gidansu da safiyar Lahadi, yayin da ‘yan bindigar suka shiga gidansu. al’umma da manyan makamai, suna harbi lokaci-lokaci.
Ya ce masu garkuwa da mutanen sun ajiye kansu ne a wurare masu mahimmanci a cikin yankin.
A cewarsa, al’ummar kauyen Sheda sun kasance cikin tashin hankali a ranar Lahadin da ta gabata, saboda harbe-harbe da masu garkuwa da mutane suka yi a wasu wurare masu muhimmanci, kafin su yi garkuwa da ma’auratan.
Ya ce shugaban ‘yan bindigar ya saki matar ne a lokacin da ake kai su dajin, inda ya bukaci ta je ta nemi kudin fansa.
DSP Adeh Josephine, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, bai amsa kiran wayar da akayi masa ba domin tabbatar da harin.