Gwamnan jihar Edo Mista Godwin Obaseki ya sake komawa ofishin uwar Jam’iyyar APC na kasa domin a sake tantance shi sakamakon karatowar zaben da za a yi a ranar 22 ga watan Yunin da muke ciki.
Da misalin karfe 1 na rana gwamna ya isa ofishin Jam’iyyar domin a tantance shi, sai dai bai samu an tantance shi ba.
Sai dai gwamnan ya sake komawa ofishin da misalin karfe 7:59 na daren nan domin tantancewar tare da wasu daga cikin mukarrabansa; daga ciki har Sanata Domingo Obende.
A wani ci gaban kuwa, mai baiwa gwamnan shawara akan kafar yada labarai Crusoe Osagie, ya bayyana cewa gwamnan ya isa ofishin uwar Jam’iyyar da wuri domin a tantance shi, amma aka ce masa kwamitin da zasu tantance shi basu shirya ba.
https://dimokuradiyya.com.ng/zan-yi-takara-a-jamiyyar-apc-gwamna-obaseki/
Obende ya ce “gwamna ya iso da wuri domin a tantance shi, amma abun mamaki sai akace kwamitin basu shirya ba, hakan ne yasa Gwamna ya tafi wani taro da kungiyar gwamnoni ta shirya da zummar yana gama taron zai kira kwamitin domin ya dawo a tantance shi”.
“Bayan kammala taron gwamna Obaseki ya kira kwamitin ta wayar tarho, amma abin mamaki basu amsa kiran nasa ba”. Cewar Obende.