A wani al’amari mai ban mamaki, Gwamna Abdullahi A. Sule na jihar Nassarawa ya bayyana rusa majalisar kwamishinoninsa da duk wasu masu rike da mukaman siyasa a yayin wani taron karawa juna sani na majalisar zartarwa (EXCO) da aka yi a gidan gwamnati da ke Lafia ranar Alhamis. Kamar yadda Daily Sun ta ruwaito.
A yayin taron, wanda ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ‘yan majalisar zartaswarsa da masu rike da mukaman siyasa, Gwamna Sule ya bayyana jin dadinsa da irin gudunmawar da suka bayar da sadaukar da kai ga jihar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Dalilin Da Yasa Buhari Ya Amince Da Cire Wasu Kudaden Kwanaki Kadan Kafin Saukarsa A Mulki – FG
Ya yaba da kokarin da suke yi na tabbatar ci gaban jihar tare da fuskantar Kalubalen suka samu lokacin aikinsu.
Gwamna Sule ya bayyana bukatar samar da ingantaccen tsarin gudanar da mulki wanda zai iya magance bukatu da burikan al’umma.
Ya jaddada kudirinsa na inganta ayyuwar Al’ummar Jihar bisa gaskiya, da tabbatar da adalci a tsakanin al’amuran jihar.
Yayin da yake sanar da rushe majalissar Zartaswar, Gwamna Sule ya tabbatar wa Kwamishinonin da masu rike da mukaman siyasan cewa za a rika tunawa da irin gudunmawar da suka bayar, kuma za a ci gaba da martaba kwarewar da suka nuna a lokacin aikin su.
Ya kuma bayyana fatansa cewa za su ci gaba da jajircewa wajen ci gaban jihar tare da bayar da goyon bayansu a nan gaba.
A wani labarin kuma, Matatar Man Dangote Zata Samar Da Dala Biliyan 21, Matasa Sama Da 100,000 Za su Sami Aiki
Shugaban rukunin kamfanin Dangote wato Aliko Dangote ya bayyana cewa sabuwar matatar Mansa mai tace Lita 650,000kowace rana, za ta dauki matasan Najeriya 100,000 aikin yi da kuma samar da sama da dala biliyan 21, don ceton wa kasar nan makudan kudaden da za a yi amfani da su wajen shigo da mai. Kamar yadda Independent Post ta ruwaito.
A cewar hamshakin dan kasuwar, kamfanin yanzu yana da ma’aikata sama da 33,000.