Wata kotun tarayya a Abuja ta yankewa Maryam Sanda hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan da aka sameta da laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello.
Mai shari’a Yusuf Halliru ya ce hukuncin wanda ya yi kisa shi ne a kashe shi, a don haka ya yanke mata hukuncin kisa.