A yunkurin jam’iyar PDP na gudanar da Taron Kwamitin zartarwa karo na 92, don ci gaba da shirye-shiryen gudanar da Babban taron ta na kasa, Masu zanga-zanga dake goyan bayan Tsohon Shugaban jam’iyar na Kasa Prince Uche Secondus da Gwamna jihar Rivers Nyesom Wike, sun afka Sakatariyar jam’iyar na kasa a yau Asabar.
Ya yin da magoya bayan Secondus suka toshe babban kofar shiga Sakatariyar, magoya bayan Gwamna Wike sun toshe dayar kofar.
Magoya bayan Secondus sun zo da rubuce-rubuce a kan Kwali, masu alaka, da “Manufar kabilar Ijaw: PDP ku ba mu hakkin mu; Ijaw ba bayin PDP bane; Uche Seconus ne ya cancanci Shugabancin jam’iyar; Gwamna Wike yana goyon bayan dan uwanshi Secondus, don kammala wa’adin mulkinsa, da dai sauran su.
KARANTA WANNAN LABARIN: Majalissar Filato ta bai wa Gwamna Lalong makwanni 2 da magance matsalar tsaro da jihar ke fuskanta
A nasu bangaren magoya bayan Gwamna Wike sun zo da rubuce-rubuce kamar haka: ” Babban ma’aikaci, al’umar Rivers suna tare da Kai”
A kwai Karin bayani…