‘Yan mata hudu da aka sace a kauyen Kautikari da ke karamar hukumar Chibok a jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya, sun samu ‘yanci a karshen mako jiiya, kamar yadda mazauna garin Chibok suka bayyana a ranar Lahadi.
‘Yan matan na daga cikin mutane 24 da aka sace a yayin wani hari da aka kai ranar 14 ga watan Janairun 2022 a kauyen Chibok inda ‘yan ta’addan suka yi awon gaba da kayan abinci da sauran abubuwan bukatun mazauna kauyen.
Chibok dai na da tazarar kilomita 150 daga Maiduguri babban birnin jihar Borno kuma ana ci gaba da fuskantar hare-hare daga bangarorin tagwayen Mayakan, lamarin da ya sa jama’a suka yi ta kuka a baya-bayan nan, suna zargin gwamnati da yin watsi da su.
Idan dai za a iya tunawa, a lokacin da lamarin ya afku, an yi garkuwa da mazauna kauyen Kautikari guda tara, kafin daga bisani ‘yan ta’addan su sako manyan mata biyu da wasu yara kana na.
Haka kuma, ‘yan matan hudu sun kai su Dille. Dille wani kauye ne a karamar hukumar Askira Uba a jihar Borno, wanda ke iyaka da dajin Sambisa. An kuma bayyana cewa kauyen ya kasance matattarar masu tayar da kayar baya a yankin.
Kautikari dai yana Gabas ne kuma mai tazarar kilomita 15 daga garin Chibok, inda akasari mabiya addinin Kirista ne. Mutanen sun ce harin da aka kai kauyen Kautikari ya fi sau 20 tun bayan da aka sace ‘yan matan Chibok guda 276 a shekarar 2014 wanda ya jawo firgici ayankin.