Shugaba Muhammadu Buhari tare da tsohon Ministan tsaro na Kasa, wato T. Y. Danjuma suna wata ganawar sirri yanzu haka a fadar shugaban kasa dake Villa a babban birnin tarayyar Kasar nan.
Janar Danjuma tsohon Ministan tsaro ne a karkashin mulkin Shubaga Olusegun Obasanjo.
Janar Danjuma ya yi kaurin suna tare da fice wajen caccakar gwamnatin Buhari musamman akan abinda ya shafi harkar tsaro.
Tsohon Ministan tsaron ya kalubalanci gwamnatin tarayya da sojin kasar nan wajen nuna halin-ko-in-kula akan rikicin Fulani a fadin tarayyar kasar nan.
A yayin jawabinsa a Jami’ar Ibadan, Danjuma ya kalubalanci Kabilar Yoruba, kan cewa suna tsoron fadawa wannan gwamnatin gaskiya.
Danjuma ya kara cewa ‘yan Najeriya ba zasu uya barci ba da zarar ya bayyana irin abubuwan dake faruwa a kasar nan.
A wata tattanauwa da aka yi da Buhari ya bayyana cewa sukar da Danjuma yake yiwa gwamnatinsa bata da wata fa’ida fiye da mutanen da suka zabe sa a shekarar 2019.
Buhari ya kara da cewa ‘yan Najeriya sun aminta da shi da kuma irin tsarin mulkinsa shi yasa suka sake basa dama domin sake jagorantar kasar nan a karo na biyu.
Daga: Abubakar Muhammad Usman