Hajiya Yar-Sokoto Jega, shugabar mata ta jam’iyyar PDP mai wakiltar Kebbi ta tsakiya a jihar Kebbi, ta koma jam’iyyar All Progressives Congress (APC).
Jega ta bayyana haka ne a lokacin da ta ke jawabi a wajen wani biki a Birnin Kebbi a ranar Laraba.
A cewarta, ta bar jam’iyyar ne saboda rashin adalci da kuma rashin shugabanci na gari.
Jega ta bayyana cewa ta yanke shawarar komawa jam’iyyar APC ne saboda dimbin nasarorin da Gwamna Atiku Bagudu ya samu, inda ta kara da cewa ta koma jam’iyyar ne da magoya baya sama da 800.
Ka gargadi magoya bayan ka – Tinubu ya ja kunnen Peter Obi kan yada labaran karya
“Na shafe shekaru da yawa a PDP, ba su da wani abin da za su nunawa mutane kuma jam’iyyar ta yi watsi da mu.
“Ni ma ina amfani da kudina wajen tafiyar da jam’iyya, amma duk da haka ban ga wani sauyi da jama’ata ta samu ba, musamman matan da nake wakilta.
“Kafin sauya sheka na, ina shugabancin kananan hukumomi takwas a karkashin jam’iyyar PDP, na tafi tare da mafi yawan mabiyana,” in ji Jega.
Wasu daga cikin manyan baki da suka halarci bikin sun hada da Alhaji Abubakar Kana-Zuru, shugaban jam’iyyar APC na jihar Kebbi; Alhaji Sani Zauro, shugaban kungiyar dattawan APC na jiha; da Alhaji Faruk Musa-Yaro, Mataimakin Gwamnan Jihar.
A wani labari kuma na daban.
Manyan Jami’an Amurka sun firgice, yayin da Rasha ta harba tauraron dan adam din Iran
Ƙasar Rasha ta yi nasara kaddamar da har ba Tauraron ɗan adam na kasar Iran zuwa sararin samaniya duk kuwa da damuwar da Amurka ta nuna kan buƙatar yin hakan.
An kaddamar da Tauraron Ɗan adam din ne mai suna Khayyam a Baikonur da ke cikin Kazakhstan.
A makon da ya gabata Manyan Jami’an Amurka sun bayyana wa Jaridar Washington post cewa suna fargabar kada Rasha ta yi amfani da Tauraron wurin leken assirin sojojin Ukraine, amma kuma Iran tace za a yi amfani da shune wurin kula da muhallin kasar kuma gwamnatin Iran ce zata kula dashi.
Rasha ta dai dade tana kokarin neman nasara a yaƙin da ta keyi a Ukraine yayin da mahukunta suke zargi Hukumar kula da yanayin Rasha da faɗa wa Gwamamnatin Iran cewa su zasu kula da Tauraron ɗan adam tsawon watanni domin taimakamata a yaƙin da ta keyi.
Majiyar Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito wata majiya da ta bukaci a sakaye sunan ta, ta bayyana cewa, tauraron dan Adam din, yana iya baiwa ƙasar Iran da Rasha damar amfani da Tauraron domin kula da ayyukan soji da wurin da sojojin kasashen ke zaune.
Sai dai wata sanar wa da Iran ta fitar, ta karyata wasu hotuna da aka yada dake nuna amfani da tauraron wurin ayyukan soji.
Gwammanatin iran tace tuni Hukumar kula da sararin samaniyar ƙasar ta karbi bayanai farko akan tauraron dan Adam din.
Harba tauraron dan Adam din ya zo ne makonni uku bayan da shugaba Vladimir Putin ya ziyarci shugaban addinin kasar Iran Ayatollah Ali Khamenei a birnin Tehran.
Haka kuma, Lamarin yazo dai dai da lokacin da ake kara samun zaman dar-dar tsakanin Amurka da Iran, bayan da kungiyar tarayyar Turai ta bayar da bayanenta na karshe da ke neman sake sabunta yarjejeniyar Nukiliyar Iran.
A yanzu dai zabi ya ragema manyan jami’an gwamnati Amurka na su sanya hannu ga bayanan da aka gabatar musu na yarjejeniyar ko kuma su yi buris da shi.
Shi dai tauraron dan adam din na Khayyam an rada masa suna ne domin tunawa da fitaccen marubucin nan kuma masanin tsarin rayuwar dan adam na yankin Pasha Omar Khayyam.