Kungiyar kwallon kafa ta Tottenham Hotspur ta sanar da korar Kocinta Nuno Espirito Santo
Hakan ya biyo bayan rashin nasara da kungiyar tayi a hannun Manchester United a gida da ci 3-0 a karshen mako.
“Kungiyar ta sanar da cewa, ta sallami Nuno Espírito Santo a yau, tare da Masu taimakamawa da suka hadar da: Ian Cathro, Rui Barbosa da kuma Antonio Dias,” in ji Tottenham a shafinta na yanar gizo.
Fabio Paratici, Manajan Daraktan gudanarwar kungiyar Kwallon Kafar, ya ce, “Na san yadda Nuno da sauran masu taimaka masa, suke son yin nasara kuma na yi nadama cewa, ya zama dole ne mu dauki wannan matakin.
KARANTA WANNAN LABARIN: Gwamnatin Zamfara ta Bude Kasuwannin Mako-mako
“Nuno mutum ne na gaskiya kuma koyaushe za a yi maraba da shi a nan gaba. Ya kamata mu gode masa, tare da mataimakansa da yi musu fatan alheri a nan gaba.”
Sanarwar ta kara da cewa, “Za’a sanar da Wanda Zai gaji Cocin Nan gaba kadan.”
Comments 1