Akalla masu ibada biyu ne aka kashe tare da yin garkuwa da da dama bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari cocin Baptist da ke Kakau Daji a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna a ranar Lahadi.
Mummunan lamarin ya faru ne a lokacin da suke tsaka da ibada a jiya Lahadi 31 ga Oktoban shekarar 2021.
‘Yan bindigan sun kewaye cocin kafin su fara harbi ba kakkautawa.
Shugaban kungiyar Baptist ta Kaduna Ishaya Jangado, wanda ya tabbatar wa majiyar jaridar Dimokuradiyya harin, ya ce, an kuma yi awon gaba da wasu da ba a tantance adadinsu ba a yayin harin.
KARANTA WANNAN LABARIN: ABun da Bazan taba Mantawa ba, inji Farida Jalal
“Al’amarin ya faru ne da safiyar jiya Lahadi, amma ba mu san ainihin adadin mutanen da aka yi garkuwa da su ba tukuna,” in ji shi
Da yake mayar da martani, shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya CAN reshen jihar Kaduna, Joseph Hayab, ya bayyana harin a matsayin “wani labari mai ban tausayi na yadda rashin tsaro ya tabarbare a kasar nan.”
Ya bayyana hakane yayin da yake zantawa da manema labarai inda Kuma ya Kara da cewa,“Ana kashe ‘yan kasa kamar kaji. Waɗannan mugayen mutane sun daɗe suna damun mu.”
“Ina jajanta wa iyalan kungiyar Baptist da Kiristocin Kaduna bisa wannan rashi da aka yi, ina kuma kira ga hukumomin tsaro da su ci gaba da yakar makiya ’yan Najeriya da siyasa. Babu wanda ya san wanda za a kai wa hari a nan gaba.” a cawar shi.
Karamar hukumar Chikun dai na daya daga cikin yankunan da gwamnatin jihar Kaduna ta dakatar da sadarwa domin yaki da ‘yan bindiga da garkuwa da mutane a fadin jihar.