Wakilinmu Shu’aibu Ibrahim Gusau
Tsohon gwamnan jihar zamfara, Abdul’aziz yari Abubakar ya karyata zargin da ake Masa na ya bar bashin sama da Biliyan 251.
Tsohon gwamnan ya karyata zargin ne cikin wata takarda da Mai bashi shawara kan harkar yada labaru, Hon. Ibrahim magaji Dosara, ya karantawa manema labaru a sakatariyar ofishin jam’iyar APC da ke Gusau, Babban Birnin Jihar.
Tsohon gwamnan ya ce shi be bar bashin ko sisi ba, sai dai ya bar zunzurutun kudi har naira Biliyan Bakwai ga sabuwar gwamnati .
Ya Kara da cewa duk abinda kwamitin karbar mulki, Wanda shugabanta tsohon Mataimakin gwamna Ibrahim wakkala ya bayyana karya ce kawai Kuma ba wani abu yasa yayi hakan ba sai domin ya Bata Masa suna kawai.
Yari ya ce duk wani harkar kwangila daya gudanar da harkar fanshon ma,aikata babu Wanda hakkin abin yake kansa sai Ibrahim wakkala.
Sai dai wannan dambarwar da ta kunno Kai a jihar zamfara ya daurewa al’ummar jihar Kai domin Wakkala, ya bayyana cewa wannan bashin da suka bayyana shine Wanda kwamitin Mika mulki ta Basu.
Domin a cewarsa mutane suna ta yayata Biliyan Dari aka bari a yanar gizo, don haka ya ce zasu fito da nasu binciken idan suka kammala, idan kuma akwai bukatar su gayyaci Yari, don ya bayyana a gaban kwamiti to zasu gayyaceshi.
A lokacin karanta wannan sako na Yari, Hon magaji Dosara, ya Sami rakiyar shugaban jam’iyar APC, Lawal Liman, da sakataren jam’iyar ta APC Sani Mono, da tsohon kwamishina Ibrahim muhammad Birnin Magaji, da dai sauransu.