A yau Lahadi ake gudanar da zaben sabon shugaban kasar Tunsiya. Sama da mutum milyan 7 ne suka cancanci kada kuri’unsu a zaben shugabancin kasa da ake gudanarwar din.
Mutum 24 ne ke takara domin maye gurbin shugaba Caid Essebsi wanda ya rasu a cikin watan yulin da ya gabata.
An tsara bude rumfunan zabe da misalin karfe 8 na safe kafin a rufe a 6 na yamma domin bai wa jama’a damar kada kuri’unsu a wannan zabe mai cike da tarihi, lura da cewa Tunisia, ita ce kasar Larabawa ta farko da aka samu barkewar bore a shekara 2011 sannan aka gudanar da zabe irin na dimokuradiyya a cikinta.