Tsohon shugaban majalisar wakilai, Yakubu Dogara, ya yi watsi da labarin da ake cewa yana da burin tsayawa takarar kujerar mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen shekara ta 2023.
A kwanakin da suka gabata ne Dogara ya ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC, inda ya bayyana sabanin ra’ayin siyasa tsakaninsa da Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad na jam’iyyar PDP, a matsayin dalilinsa na sauya sheƙar.
Tun bayan haka ne mabiya kafafen sada zumunta suka rika yaɗa jita-jitar manufar da ta sanya tsohon shugaban majalisar wakilan ya sauya sheƙar zuwa APC bayan wani ɗan taƙaitaccen zango da ya shafe a babbar jam’iyyar adawa.
https://dimokuradiyya.com.ng/yanzu-yanzu-dogara-ya-koma-apc-bayan-ganawa-da-buhari/
Sai dai Dogara cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi ta bakin mai magana da yawunsa, Turaki Hassan, ya ce jita-jitar ta samo asali ne daga ’yan adawa masu neman ɗauke masa hankali.
Sauyin sheƙarsa daga jam’iyyar PDP zuwa APC ta haifar da tababa a tsakanin al’ummar mazaɓarsa ta Dass da Tafawa Balewa da Bogoro a Jihar Bauchi.
A yayin da aka samu rabuwar kai a tsakanin al’ummar ƙananan hukumomin uku, wasu na goyon bayan shawarar da Dogara ya yanke tare da yi masa fatan alheri, wasu kuwa suka gami da caccaka ce ta kaure a tsakaninsu da shi.