By Abbas Yakubu Yaura
Hukumar yada labarai ta kasa ta gargadi gidajen yada labarai da su guji yada labaran da ka iya kawo cikas ga hadin kan kasar, yayin da zaben Anambra zai gudana a ranar Asabar 6 ga watan Nuwamba.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai taken, ‘Zaben Anambra: NBC ta yi gargadi game da yada shirye-shiryen da ka iya kawo cikas ga hadin kan Najeriya, wanda Darakta Janar na hukumar ta NBC, Balarabe Ilelah, ya sanya wa hannu a ranar Alhamis.
Ilelah ya umurci duk masu yada labaran zaben gwamna da su bi ka’idojin zabe da aka tanada a kundin tsarin yada labaran Najeriya.
Sanarwar ta ci gaba da bayyana wasu daga cikin dokokin da masu watsa shirye-shirye zasu bi, inda ta kara da cewa bai kamata a yi hasashen sakamakon zabe ba bisa ka’ida ba a dandalinsu.
Dokar ta kara da cewa, “5.3.3 (j) tabbatar da cewa watsa yakin neman zabe na bangaranci, jingle, sanarwa da duk wani nau’i na tantance jam’iyyar siyasa ko alama yana karewa sa’o’i ashirin da hudu kafin ranar zabe, kar a yi amfani da duk wata ƙuri’ar da aka samu a wurin jefa ƙuri’a ko daga rumfunan zaɓe don tsara ko hasashen yiwuwar ɗan takara;
Kazalika “5.3.3 (k) ta mika sakamakon zabe ko bayyana wanda ya yi nasara kamar yadda jami’in zabe mai izini na zaben ya sanar.”
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Hukumar tace masu watsa shirye-shiryen da suka saba wa tanade-tanaden za su fuskanci hukunci mai tsanani.