Gwamnan Jihar Edo Mista Godwin Obaseki, ya bayyana a gaban kwamitin tantance ‘yan takarar zaɓen fidda gwanin gwamnan jihar Edo, na sabuwar jam’iyyarsa ta PDP a Abuja.
Kwamitin Hon. Kingsley Chinda na tantance Obaseki ne domin shiga takarar washegarin ranar da Gwamnan ya koma jam’iyyar.
Obaseki ya shiga jam’iyyar PDP ne wadda ta ba shi damar neman takara ne bayan tsohuwar jam’iyyarsa ta APC ta hana shi.
https://dimokuradiyya.com.ng/da-dumi-dumi-gwamnan-jihar-godwin-obaseki-ya-koma-jamiyyar-pdp/
Bayan shigarsa jam’iyyar a kurarren lokaci, jam’iyyar ta kara dage zaben fidda gwanin zuwa Alhamis 25 ga watan Yuni.
Sai dai wasu masana harkar siyasa na ganin cewa dage zaɓen, na iya bawa gwamnan dama wajen ganin yayi mai yiwuwa don ganin jam’iyyar ta PDP ta tsayar da shi a matsayin ɗan takararta a zaɓen mai zuwa.