Hukumar lura da aikin Hajji ta jihar Katsina, ta nemi maniyyata aikin Hajji na shekarar 2021 da su yi harramar fara biyan kudin Hajjin, inda suka nemi da su hanzarta hukumar domin fara rijistar zuwa Hajjin.
Hukumar ta ce su zo ofishinsu domin bada naira dubu dari biyar a matsayin shigar kudi. Daraktan hukumar, Alhaji Suleiman Nuhu-Kuki, ne ya bayyana hakan a taron manema labarai a Katsina a ranar Lahadi.
Daraktan ya tabbatar da cewa; gwamna Aminu Masari ya amince da maniyyata su fara biyan naira dubu dari biyar domin fara cike gurbi da hukumar Hajjin ta kasa, NAHCON ta bai wa jihar.