Wakilinmu Ahamed Musa Gumel
Gwamnatin jihar Jigawa zata gina masallacin mata a jami’ar gwamnatin tarayya ta Dutse akan kudi fiye da naira miliyan 57.
Shugaban hukumar bada tayin kwangilar a ofishin Sakataren gwamnatin jihar kuma babban Sakataren kudi da mulki na ofishin sakataren gwamnatin jiha Alhaji Muhammad K-Dagaceri ya sanar da hakan a wajen bikin bude tayin bada kwangilar gina sabon masalacin.
Yace kamfanoni uku ne suka nuna shaawarsu ta gudanar da aikin gina masallacin.
Alhaji Muhammad Dagaceri daga nan ya yi kira ga wanda Allah ya ba nasarar aikin ya tabbatar da yin gaskiya da adalci da kuma aiki mai inganci.
Ya kuma hori kamfanin da ya samu nasara ya tabbatar ya kammala aikin lokaci.
A nasa jawabin wakilin babban Daraktan hukumar kula da bada ayyukan kwangila na jihar Jigawa Injiniya Nura Jibo yace tsarin gwamnatin Jigawa ne ya tantance duk wani kamfani da zai gudanar da aikin kwangilar domin ganin an yi aiki mai inganci.
Ya kuma baiwa masu neman kwangilar tabbacin yin gaskiya da adalci wajen tantancesu.
Daya daga cikin kamfanonin da suka shiga neman kwangilar wakilin kamfanin Modang Investment Limited Alhaji Garba Isma’il ya baiwa gwamnatin jiha tabbacin cewa muddin kamfaninsu ya samu kwangilar zai gudanar da aiki mai inganci cikin lokacin da aka kayyade.