Gwamnatin jihar Zamfara ta ce za ta ba ɓarayin daji saniya biyu kan kowace bindiga ɗaya da suka miƙa, a wani mataki na yunkurin kawo karshen matsalar tsaro da jihar ke fama da ita.
Gwamnan jihar Bello Matawale ya bayyana shirin ne yayin da ya karɓi baƙuncin Babban Sufeto na ‘ƴan sandan Najeriya Mohammed Adamu da Shugaban hukumar tsaron farin kaya DSS Yusuf Bichi waɗanda Shugaban Nijeriya ya tura jihar saboda tabarbarewar tsaro.
To sai dai gwamnatin na ci gaba da jan hankulan mutane a ciki da wajen Najeriya, yayin da masana ke cewa a yi hattara.
Kwamishinan tsaro na jihar Zamfaran Abubakar ya tabbatar wa da BBC cewa gwamnan ya bujiro da wannan mataki ne don rage yawaitar makamai a hannun mutane.
Shafin na BBC ya kuma labarto cewa; gwamnan ya ce za su bai wa ɓarayin shanun biyu-biyu ne sakamakon Fulani sun fi buƙatar su a kan tsabar kuɗi.